On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

Malaman Kwalejin Ilimi Ta Bichi Sun Zargi Hukumar Makarantar Da Karkatar Da Naira Milyan 34

Kwalejin ilimi Ta Gwamnatin Taraiyya Dake Bichi

Kungiyar Malaman kwalejin ilimi ta gwamnatin taraiyya dake Bichi a nan Jihar kano,Ta zargi hukumar gudanarwar makarantar da karkatar da wasu kudade wanda Asusun tallafawa manyan makarantu Tetfund ya baiwa makarantar har naira milyan 34 domin biyan hakkokin Alawus na masu sanin makamar aikin koyarwa,domin warware wani batu da ya taso daga hukumar nan ta EFCC.

Kungiyar ta baiyana  cewar  a  baya  hukumar yaki da masu yiwa  tattalin arzikin kasa  zagon kasa  EFCC  ta tilastawa  Kwalejin ilimin  ta  biya  dan kwangila  wasu kudade  amma daga  baya  ta yanke  shawarar  karkatar da kudin na  Tetfund domin biyan wasu  bukatu  na daban

Shugaban Kungiyar  Malaman kwalejin ilimi ta gwamnatin taraiyya  dake  Bichi a nan  Jihar  kano  Dr  Hussaini  Yahya ya  baiyana  kwalejin a matsayin  tamkar  wata  Sakandire  saboda  yanayin tabarbarewa  data samu kanta a ciki, Inda  ya koka  kan yadda  Daliban makarantar  da kuma Malamai  basu  da wani katin shaida  dake  tabbatar  su dasu a matsayin ‘yan makaranta

Bugu da kari  ya  ce  a Alhamis din  makon jiya  ne  kungiyar  ta shiga  yajin aikin sai baba ta gani saboda matsalolin da suka shafi   rashin saka  kudi a asusun biyan fansho da sauran wasu matsaloli wanda  har kawo  yanzu  babu  wani mataki da  makarantar  ta dauka akan  wannan batu.

 

To sai dai kuma  a martanin da shugaban Kwalejin Ilimi  ta gwamnatin taraiyya dake  garin Bichi a nan jihar Kano, Farfesa  Muhammed  Fagge ya mayar ,  Ya  baiyana  zargin karkatar da kudin da  malaman suka yi a matsayin wata  jita-jita,  Yana mai cewar dole  ne a biya  malaman da abun ya shafa  hakkokinsu.

Kazalika  ya zargi  kungiyar  da rashin bin ka’idar  data dace  kafin  tafiya  yajin  aikin  da suka  fara  a makon jiya

Dangane da maganata  ta  ID Card Kuwa, Shugaban makarantar  ya baiyana cewar  kwalejin  tana katin shaida da  take  dashi, Sai dai akwai bukatar a sake  inganta shi , Sai dai kuma ya  ce  kokarin yin hakan ya gamu da cikas, saboda  rashin hadin kai da aka samu.

Farfesa  Muhammed  Fagge  Ya  ce rashin saka kudi a cikin asusun biyan fansho  ya samo  asali ne daga  tsarin nan  na biyan kudi da gwamnatin taraiyya  ke  amfani dashi  na IPPIS, Kuma kungiyar tana sane  da irin kokoarin da aka yi domin magance  matsalar.