Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya bukaci shugabannin duniya dasu jingine banbancin dake tsakaninsu tare da yin aiki tare, domin murkushe aiyukan ta’adanci a nahiyar Afrika.
Osinbajo ya yi wannan kiran ne a ranar Talata a yayin wata mukala da aka gabatar a kwalejin Kings dake birnin London,inda ya koka kan yadda aiyukan ta’addanci suka yi kamari a yankin Sahel na Afrika.
Ya baiyana cewar aiyukan ta’adanci sun haifar da tarin matsaloli,inda y ace kamata yayi shugabannin duniya su fahimci cewar matsalar aiyukan ta’adanci a wani bangare na duniya, matsala ce data shafi dukkanin ‘yan adam.
Bugu da kari mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya yi kira da a kawo karshen rikicin dake faruwa tsakanin kasashen Rasha da Ukrain,tare da yin kira ga kasashen Afrika dasu tashi haikan wajen ganin sun dogara da kansu ta bangaren samar da abinci.
Comments
Add a comment