On Air Now

ZANGON MARAICE

3:00pm - 8:00pm

Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osinbajo Ya Koka Kan Matsalar Aiyukan Ta'adanci A Nahiyar Afrika

Osinbajo

Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya bukaci shugabannin duniya dasu jingine banbancin dake tsakaninsu tare da yin aiki tare, domin murkushe aiyukan ta’adanci a nahiyar Afrika.

Osinbajo  ya yi wannan kiran ne  a ranar Talata  a yayin wata mukala da aka gabatar a kwalejin  Kings dake birnin London,inda ya koka kan yadda aiyukan ta’addanci  suka yi  kamari a yankin Sahel na Afrika.

Ya baiyana cewar  aiyukan ta’adanci sun haifar da tarin matsaloli,inda  y ace  kamata yayi shugabannin duniya su  fahimci  cewar  matsalar  aiyukan ta’adanci a wani  bangare na duniya, matsala ce  data  shafi dukkanin  ‘yan adam.

Bugu da kari mataimakin shugaban kasa  Yemi Osinbajo ya yi kira  da a kawo karshen rikicin dake faruwa tsakanin kasashen Rasha da Ukrain,tare da yin kira ga kasashen Afrika  dasu tashi haikan wajen  ganin sun dogara da kansu ta bangaren samar da abinci.

 

 

 

 

 

 

Comments

Add a comment

Log in to the club or enter your details below.

A Biyo Mu a Shafukan Sada Zumunta

Today's Weather

  • Kano

    Sunny intervals

    High: 37°C | Low: 23°C