On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Na Dauki Kwana Biyu Ban Rintsa Ba Domin Nasarar Akpabio

SANATA BAMIDELE

Daraktan yakin neman zaben Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa na goma, Sanata Opeyemi Bamidele ya ce sanatocin da ke muradin ganin Godswill Akpabio ya samu nasara, sun hallara zauren majalisar dattawa tun da karfe 4 na Asubahin jiya, domin dakile irin abunda ya faru a zaben shugaban majalisar dattawa na shekarar 2015.

Idan ba’a manta  ba a shekarar  2015,  Sanatocin dake goyon bayan tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, Suka yi zaman dirshan a zauren majalisar dattawan domin tabbatar da nasarar  tsohon gwamnan jihar Kwara a  matsayin shugabansu, A yayin da ragowar sanatocin ke ganawa da  shugaban kasa Buhari a daidai lokacin da aka rantsar da sabon shugabancin majalisar.

Da yake jawabi a yayin wata liyafa da aka shirya masa domin murnar komawarsa zauren majalisar dattawa a karo na biyu, Sanata Bamidele dake wakiltar Ekiti ta tsakiya, Ya  ce  ya dauki tsawon kwanaki biyu batare da ya rintsa ba,  domin tabbatar da nasarar  Sanata Godswill Akpabio.