On Air Now

ZANGON SAFIYAR LAHADI

5:00am - Noon

Najeriya Ta Biya Dala Dubu 30 Kan Kowace Motar Safa Guda 40 Da Suka Kwaso 'Yan Najeriya Zuwa Masar

SANI GWARZO

Kawo yanzu gwamnatin taraiyya ta baiyana cewar ta kashe zunzurutun kudi har Dala Milyan 1 da Dubu 200 domin yin hayar motocin Safa wadanda zasu kwaso ‘yan Najeriyar da suka makale daga kasar Sudan mai fama da yaki zuwa iyakon kasar Masar , wanda kuma daga nan ne za’a dauko su ta cikin jirgi zuwa gida Najeriya.

Babban sakatare  a ma’aikatar kula da harkokin Jin kai da kare  afkuwar  Bala’oi  ta kasa, Nasir  Sani Gwarzo  ne  ya baiyana  haka, jim kadan bayan kammala  wata ganawar  sirri  a  ma’aikatar dake Abuja.

Ya  ce  daga cikin motocin Safa  40 da aka yi amfani da su domin kwaso  ‘Yan  Najeriyar da suka makale a  Sudan, An biya kowace  Mota  daya  Dala Dubu 30.

Ya kara da cewar  tsaikon  da  ‘yan Najeriyar  suka fuskanta akan iyakokin kasar  Masar  ya biyo bayan  cika  sharuddan  babban bankin kasa,  Yana  mai cewar  babu yadda  za’a yi a  tura  kudi kai tsaye  zuwa  kasar  Sudan,Dole  ne  sai anyi amfani da Dan kai  sako.