On Air Now

ZANGON DARE

8:00pm - Midnight

Nasarar Oyebanji Zabin Allah Ce -Dan Takarar PDP A Zaben Ekiti Olabisi Kolawole

‘Dan takarar jam’iyyar PDP a zaben gwamnan jihar Ekiti, Olabisi Kolawole, ya taya dan takarar jam’iyyar APC Biodun Oyebanji murnar nasarar da ya samu a zaben.

Baturen zaben Kayode Oyebode, shine ya ayyana Oyebanji a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna na jihar ta  Ekiti da  safiyar ranar Lahadi.

A cikin wasikar taya murna, Kolawole ya yi fatan Allah ya ba Oyebanji nasara wajen tafiyar da mulkinsa, inda ya ce nasararsa zabin Allah ce, domin mulki nasa ne.