Hukumar kimiyyar ruwa ta ‘Kasa ta fitar da gargaɗin yiwuwar ambaliya na kwanaki bakwai, tana mai cewa akwai matsakaicin haɗarin ambaliya a jihohi 17 tsakanin 21 zuwa 27 ga watan Yuli.
Hukumar ta ce gargaɗin ya biyo bayan tumbatsarruwa a manyan wuraren da ake sa ido da koguna, al-amarin da ke ƙara yiwuwar ambaliyar.
Darakta Janar na hukumar kimiyyar ruwa, Umar Mohammed, ne ya bayyana hakan a cikin Takardar Shawarar Ambaliya ta Ƙasa da aka fitar a jiya.
Ya lissafo jihohin da abin ya shafa da suka haɗa da Adamawa, Bauchi, Benue, Borno, Edo, Gombe, Imo, Jigawa, Kaduna, Kano, Kebbi, Nasarawa, Neja, Filato, Taraba, Yobe da Zamfara.
Comments
Add a comment