On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Sanata Kwankwaso Yayi Bayanin Dalilan Da Suka Ba'a Cikawa Shekarau Wasu Bakatunsa Ba

KWANKWASO DA SHEKARAU

Dan takarar shugaban kasa a karkashjin jam’iyyar NNPP Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana dalilin da ya sa jam’iyyar ta kasa cika wasu daga cikin bukatun da tsohon gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya gabatar masa.

Kwankwaso Ya shaida wa BBC Hausa cewa babu wata baraka tsakaninsa da Shekarau, wanda  shine  dan takarar kujerar Sanatan Kano ta tsakiya a jam'iyyar.

Kwankwaso ya mayar da martani ne kan labarin dake  cewa Shekarau na iya sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP saboda rashin cika sharuddan yarjejeniyar da suka cimmawa  tsakaninsu  kafin komawar Shekarau zuwa jam’iyyar NNPP.

Kwankwaso ya ce babu wata yarjejeniya da ba a cika ba tsakaninsa da shekarau, sai dai abunda ya shafi  ta ‘yan takara domin galibin mutanen da Shekarau ya kawo domin dorasu akan takarar  abun ba zai yuwu ba a lokacin sakamakon  kurewar  lokaci, la’akari da ka’idar da hukumar zabe ta shimfida.

A wani bangaren kuma,Dan takarar shugabancin kasar nan a karkashin  na jam'iyyar  NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya amince da nadin Dr. Abdulmumin Jibrin Kofa da Barista Ladipo Johnson a matsayin masu magana da yawun yakin neman zaben sa.

Wata sanarwa da mai magana da yawun Kwankwaso, Ibrahim Adamu ya fitar a ranar Laraba, ta ce Dr Abdulmumin Jibrin Kofa, wanda ya kasance  tsohon dan majalisar wakilai ne a kananan hukumomin Kiru da Bebeji, yana da gogewa a fannin gudanar da yakin neman zabe da kuma hulda da jama’a.

A cewar sanarwar, shima  Barister  Ladipo  Johnson fitaccen mai sharhi kan al’amuran yau da kullum ne  kuma tsohon dan takarar gwamna da na majalisar wakilai a jihar Legas.

Ya kammala karatunsa na digiri a Jami'ar Jihar Legas  sannan kuma shine  shugaban wata kungiya mai rajin samar da cigaba ta Johnson.