On Air Now

ZANGON DARE

8:00pm - Midnight

Shugaban Kasar Burundi Ya Sauke Firiyiministan Kasar Saboda Zargin Kulla Masa Juyin Mulki

SHUGABAN KASAR BURUNDI

Shugaban Kasar Burundi Evariste Ndayishimiye ya sauke Firiyiministan kasar tare da wani babban hadiminsa daga kan kujerunsu a yau Laraba, bayan wani gargadi na yunkurin yi masa juyin mulki da aka yi.

Ya sauke firiyiministan mai suna  Alain Guillaume Bunyoni da kuma shugaban fadar gwamnatinsa Janaral Gabruek Nizigama.

A wani taron gaggawa da  Majalisar ministocin kasar ta kirawo,  ta amince da nada Ministan tsaro na aksar Gevais Ndirakobuca a matsayin wanda zai maye gurbin firiyiministan bayan da aka kada masa kuri’a 113.