On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Tsohon Mataimakin Gwamna A Jihar Nasarawa Ya Shaki Iskar 'Yanci

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Nasarawa, Farfesa Onje Wado da aka yi garkuwa da shi a yanzu ya kubuta.

Wado, wanda aka yi garkuwa da shi daga gidansa da ke Rinza a daren ranar Alhamis, ya kubuta ne bayan ya biya Naira miliyan 4 a matsayin kudin fansa.

Wata majiya daga danginsa ta ce masu garkuwa da mutanen sun bukaci a biya su kudin fansa Naira miliyan 70, amma dangin sun tattauna kuma a karshe suka biya Naira miliyan 4 kafin a sako shi.

Shima wani tsohon kwamishinan yada labarai a jihar  Dogo Shamma ya tabbatar da sakin Farfesa  a daren jiya.