On Air Now

Off Air

Noon - 6:00pm

Wani Karamin Yaro Ya Harbe Yara 8 Tare Da Wani Mai Gadi A Sabiya

An tabbatar da mutuwar wasu kananan yara takwas tare da wani mai gadi bayan wani yaro dan shekara 14 ya bude wuta a wata makaranta da ke Belgrade, babban birnin kasar Sabiya. Kazalika an samu wasu kananan yara da ma’aikata da dama sun samu raunuka.

Kakakin ‘yan sandan  birnin  Belgrade, Veselin Milic,  ya ce wanda ake zargi  da aikata  ta’adin ya kira  hukumomi  domin su  kama shi a  harabar  makarantar.

Milic ya ce maharin ya shirya  kai harin  wata guda  da  ya gabata, kuma  an gano cewar  bindigar  da  yaron ya yi amfani da ita  ya dauko ta  ne  daga  inda  mahaifinsa  yake  ajiye   bindigar.

Ministan ilimi na  kasar  Serbia Branko Ruzic, ya bayyana kaduwarsa kan  faruwar harin  ta’addancin, inda ya alakanta  faruwar  lamarin   da tasirin kafofin sadarwa ke dashi  da  kuma  wasanni  tare da kallon fina-finai  na kasashen  turai  da ake  yi.

A yanzu haka  an ayyana zaman makoki na tsawon kwanaki uku a fadin kasar  ta  Sabiya.