Wasu 'yan bindiga sun yi garkuwa da shugaban Makarantar Firamare ta Nomadic da ke Igbojaye, Budo a ƙaramar hukumar Itesiwaju ta Jihar Oyo, Kolawale Mathew Owoade, mai shekaru 60.
Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Asabar tsakanin ƙarfe biyar zuwa shida, inda masu garkuwar suka nemi a biya su kuɗin fansa na naira miliyan 30.
Ɗansa, Abiola Owoade, ya ce mahaifinsa na kan hanyarsa ta dawowa daga gonarsa da ke Budo Aare lokacin da maharan suka tare shi. Ya ƙara da cewa masu neman sa sun gano baburinsa cikin daji a ranar Lahadi.
Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan Jihar Oyo, Olayinka Ayanlade, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa jami'an tsaro na ci gaba da ƙoƙarin ceto shugaban makarantar.
Comments
Add a comment