On Air Now

ZANGON DARE

8:00pm - Midnight

'Yan Majallisar Dokokin Jihar Kano Ta 10 Zasu Karbi Horon Sanin Makamar Aiki

A yau Alhamis 8 ga watan Yuni 2023 da karfe 11 na safe ne gwamnatin jihar Kano ta shirya taron sanin makamar aiki ga ‘yan majalisar dokoki ta 10 da zai gudana a harabar majalisar dake sakatariyar Audu Bako.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai namajalissar Uba Abdullahi ya fitar.

Ya yi nuni da cewa, horon sanin makamar ga sabuwar majalissar nada  nufin taimakawa ‘yan majalissar da dabarun ayyukansu na yau da kullum na dokoki da wakilci da sa ido wanda shi ne muhimmin aikin wakilan.

Sanarwar tayi kira ga daukacin ‘yan majalissar ta 10 da su halarci taron saboda muhimmancinsa.