On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Za'a Ci Gaba Da Aikin Titina Masu 5Kilomiter A Kanan Hukumomin Kano

ABBA KABIR YUSUF

Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da sake bude cibiyoyin koyon sana’oin dogaro da kai guda 26 da gwamnatin data gabata ta rufe su.

Kwamishinan  aiyuka da gidaje na jihar Kano, Alhaji Marwan Ahmad, Ya  baiyana cewar an samar da cibiyoyin ne a zamanin tsohon gwamnan jihar kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso domin ganin mata da matasa  sun koyi sana’oi daban daban.

Ya kara da cewar  cibiyoyin zasu taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalar shaye-shaye da  sata a jihar nan.

Ya kuma baiyana cewar  gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf  ya  umarci ‘yan kwangilar da suke aikin shimfida titi  mai tsawon kilomita biyar a daukacin kananan hukumomin jihar Kano, da su dawo bakin aikinsu  batare da bata lokaci  ba.

Hakazalika  ya ce an dawo ci  gaba da aikin  ruwan  Jakara dake cikin birnin kano wanda shima tsohuwar  gwamnati ta yi fatali da shi.