On Air Now

ZANGON DARE

8:00pm - Midnight

Za'a Daure Dalibin Da Yaki Biyan Lamunin Karatu Da Aka Bashi

Shugaban kasa

Kudirin dokar bada lamunin karatu ka daliban manyan makarantun kasar nan, da shugaban kasa Bola Tinubu ya rattaba ma hannu a jiya, Ta yi tanadin daurin shekara biyu ko biyan tarar naira dubu 500 ko kuma kuma a hadawa mutum duka,ga duk Dalibin da aka samu da lefin kin biyan bashin ko kuma saka wani yaki maida rancen da aka bashi.

Kazalika itama, kungiyar  Dalibai ta kasa,  taga baiken  hanyoyin da aka  dauka kan yadda za’a biya bashin  ga daliban da suka karbi bashin.

Dokar  dai ta bada damar kafa wani asusun ilimi na kasa, wanda zai kasance mai iko tafiyar da harkokin  bada  bashin karatun ga dalibai a kasar nan.

Asusun zai rika karbar takardun neman samun bashin ta hannun manyan makarantun da Daliban ke karatu  a cikinsu.