Gwamnatin tarayya ta ce za a fara amfani da Rigakafin zazzabin cizon sauro ta R21 a kasar nan nan da watan Afrilun 2024.
Ministan lafiya, Dr . Osagie Ehanire shi ne ya bayyana haka a jiya yayin wani taron manema labarai da aka shirya a Abuja, a wani bangare na ranar yaki da zazzabin cizon sauro ta duniya.
Ministan wanda babban sakataren ma’aikatar, Mamman Mamuda ya wakilta ya ce Najeriya ta nemi samun rigakafin har sau ukku a jere.
Ya ce ma’aikatar tana aiki kafada da kafada da hukumar kula da lafiya matakin farko ta kasa da sauran masu ruwa da tsaki wajen tsara dabarun rarraba rigakafin zazzabin cizon sauro.
Comments
Add a comment