On Air Now

ZANGON MARAICEN LAHADI

6:00pm - Midnight

Za'a Fara Rubuta Jarabawar SSCE A Ranar Litinin Mai Zuwa

Hukumar shirya jarabawar kammala makarantun sakandire ta yammacin Afrika, WAEC, Ta ce za’a fara rubuta jarabawar kammala kammala makarantun sakandire ta SSCE daga ranar Litinin mai zuwa 8 ga watan da muke ciki zuwa ranar 23 ga watan Yunin bana a Najeriya.

Da yake yiwa manema Labarai  karin haske, Shugaban Ofishin hukumar  a nan  Najeriya, Patrick  Areghan,  Ya baiyana cewar  mutane  Milyan 1 da dubu 621 da 853  daga  makarantun sakandire  dubu 20  da 851  zasu  rubuta  jarabawar  a bana.

Ya kuma kara  da  cewar  Daliban zasu rubuta  jarabawar  ne  akan darussa  daban daban har  76, A  yayin da kwararrun manyan malaman makarantun sakandire  dubu 30, zasu yi aikin saka ido  a  lokacin rubuta  jarabawar  ta SSCE.

Daga  nan sai ya gargadi  makarantu  da  su guji  kin dora  makin  jarabawar  gwaji  ta  daliban da zasu rubuta jarabawar akan lokacin da aka tsara.