On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Za'a Fuskanci Mamakon Ruwan Sama A Kano Da Wasu Jihohin Arewa

RUWAN SAMA YANA ZUBA

Hukumar Kula da Yanayi ta kasa taja hankalin jama’ar jihar Kano da wasu jihohin na Arewacin kasar nan, dasu shirya fuskantar ruwan sama kamar dab akin kwarya nan da ‘yan kwanaki masu zuwa.

Wata sanarwa da hukumar  ta fitar a ranar  Alhamis, Ta  baiyana  cewar  a yanzu haka ana fuskantar  yawaitar  cida da gajimare  a  wasu  bangarori  na Arewacin Najeriya,   Cikinsu hadda  nan jihar Kano da Borno da Jihar Taraba da Gombe  da kuma  jihar Bauchin Yakubu.

Hukumar kula da yanayin ta kasa, A wuraren da ake samun yawaitar  cida, Za’a iya samun kadawar  iska  mai karfi  kafin saukar  ruwan sama ,wadda  zata  iya  karya  turakun wutar  lantarki da Bishiyoyi  da  kuma gine-gine.

Kazalika  hukumar  ta ja kunnen  jama’a  da su kasance  masu taka-tsan-tsan  tare da zama a cikin gidajensu musamman a lokacin da ake  samun  saukar  ruwan sama mai karfe,  domin kaucewar  fuskantar tsawa.