On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Za'a Yi 'Kasa Da Tutocin Najeriya Saboda Rasuwar Sarauniyar Ingila

TUTAR NAJERIYA

Gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin yin ‘kasa-‘kasa da dukkanin tutocin Najeriya a kasar nan da wadanda suke a ofisoshin jakadancin kasashen waje dake Najeriya a ranakun 11 da 12 ga watan Satumba domin girmamawa ga marigayiya Sarauniyar Ingila Elizabeth ta biyu data mutu a ranar Alhamis.

Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola ne ya bayyana hakan  ta cikin  wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Abuja.

An sanar da rasuwar Sarauniya Elizabeth ta biyu  da yammacin ranar  Alhamis.

Ita ce Sarauniyar  Ingila da sauran kasashen renon ingila tun  daga ranar 6 ga  watan  Fabrairun 1952, har zuwa shekarar 2022 lokacin data koma ga mahalicci.

Queen Elizabeth cropped

Marigayiya Sarauniya Elizebeth ta Biyu

Ta shafe  na shekaru 70 da kwanaki 214 tana sarautar Ingila, kuma itace wadda  tafi dadewa akan sarautar Burtaniya.