On Air Now

Maraicen Asabar

6:00pm - Midnight

ZABEN 2023 : Ina Bukatar Tsabar Kudi Naira Miliyan 70 Domin Hidindimun Zabe - Alhassan Doguwa

Shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai, Alhassan Doguwa, yace yana bukatar tsabar kudi naira miliyan 70 domin yin hidindimunsa na  babban zabe kamar yadda doka ta tanada.

Doguwa yayi magana ne a ranar Alhamis bayan ganawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadarsa ta villa dake Abuja.

Ya ce ba tare da tsabar  kudin  ba, wadanda ke neman samun kujeru a majalisar dokokin kasarnan za su sha wahala.

Doguwa dai yana magana ne akan kashe kudaden da masu neman kujeru a majalisar dokokin kasar nan kamar yadda sashe na 88 (4) na dokar zabe ya tanada, sai dai kuma dokar ba ta bayyana cewa dole ne kudaden su kasance tsaba  ba.