On Air Now

Off Air

Noon - 6:00pm

ZABEN 2023: Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Sadik Wali Amatsayin 'Dan Takarar Gwamnan Kano

Kotun daukaka kara dake Kano ta tabbatar da Sadiq Aminu Wali a matsayin dan takarar gwamnan Kano na jam’iyyar PDP zaben 2023.

A wani hukunci na bai daya da ta yanke a yau Juma’a, kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin da karamar kotun baya  ta yanke na tabbatar da Muhammad Abacha a matsayin dan takarar gwamnan jihar Kano na jam'iyyar PDP.

Lauyan Muhammed Abacha ya bayyana kudirin daukaka kara a Kotun Koli

Akwai karin bayani a nan gaba