Kwankwaso Ya Nemi Dorewar Haɗin Kan 'Yan Najeriya
Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam'iyyar (NDC) a zaɓen 2027, Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi kira da a farfaɗo da haɗin kan siyasa tsakanin Arewacin Najeriya da yankin Kudu maso Gabas.
Zaben 2027: INEC ta Amince da Atiku, 'Yan Takarar ADC 470
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ce za ta amince ne kawai da 'yan takarar da shugabancin jam'iyyar African Democratic Congress (ADC) karkashin jagorancin Sanata David Mark ya gabatar, tare da tabbatar da cewa bangaren ya riga ya tsayar da 'yan takara 471 domin mukaman zabe gabanin babban zaben shekarar 2027.
Spaniya ta Tsallaka Matakin Daf da na Karshe a Gasar Cin Kofin Duniya
Spain ta ba wadda aka fi tunanin za ta lashe gasar cin kofin kwallon kafa ta duniya, Faransa, mamaki da ci 2-0 a ranar Talata domin kai wa wasan karshe na gasar cin Kofin Duniya, bayan ta nuna kwarewar dabarun wasa da suka rusa burin Les Bleus na lashe kofin karo na uku.
Kungiyoyin Fararen Hula sun Nemi a Dakatar da Gangamin Siyasa, Kafa Dokar Hana Yaɗuwar Makamai a Kano
Haɗakar wasu ƙungiyoyin fararen hula a Jihar Kano dake rajin tabbatar da siyasa mai tsafta ta yi kira da a dakatar da duk wani gangamin siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, tana mai gargadin cewa ƙaruwar rikice-rikicen siyasa da ayyukan 'yan daba da kuma yaɗuwar makamai na barazana ga rayuka, dukiyoyi da kuma dimokuraɗiyya.
© Copyright 2026 Steam Broadcasting and Communications Limited. Powered by Aiir.