Tsoffin Daliban FGC Sun Gudanar da Zanga-Zanga Lokacin da Ministan Ilimi ke Shiga Makarantar
Kungiyar Tsofaffin Daliban Kwalejin Tarayya ta Kano (FGCOSA), ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta mutunta umarnin kotu da ya umarci bangarorin da ke rikici su cigaba da kasancewa yadda suke har sai an yanke hukunci kan shirin cefanar da wasu filayen makarantar.
Mutum Guda ya Mutu, Wasu sun Bace a Hadarin Jirgin Ruwa a Jigawa
Akalla mutum daya ya rasa ransa yayin da wasu da dama suka bace sakamakon hatsarin kwale-kwale da ya afku a kauyen Malamawa da ke 'Yan Dutse a karamar hukumar Ringim ta Jihar Jigawa.
Burnham Zai Kama Aiki a Matsayin Sabon Firaministan Birtaniya
Andy Burnham zai karbi ragamar mulki a matsayin sabon Firaministan Birtaniya a yau Litinin.
Rohoton Samun Masu Bawa 'Yan Ta'adda Bayanai a Hukumomin Tsaro ya Haifar da Cece-Kuce
Jam'iyyun adawa a Najeriya sun soki gwamnatin tarayya kan amincewar da Fadar Shugaban Kasa ta yi cewa akwai yiwuwar 'yan ta'adda sun dasa jami'an su a cikin hukumomin tsaro.
Barau Ya Rubuta Wasika Ga Nuhu Ribadu Kan Barazanar Kachalla Maha A Kano
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya rubuta wa Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu, game da barazanar da wani fitaccen shugaban ‘yan fashin daji, Kachalla Maha, ya yi na kai wa Jihar Kano hari.
Masana Sun Kare Matakin Matatar Man Dangote na Sayar da Man Fetur da Dala
Wasu masana harkokin masana'antu sun kare matakin da Matatar Dangote ta dauka na karbar dalar Amurka wajen sayar da kayayyakin albarkatun man fetur din ta.
© Copyright 2026 Steam Broadcasting and Communications Limited. Powered by Aiir.